Daga Baban Khausar Imam
Tun Bayan da aka Shiga Ce-Ce-Ku- Ce Game da Tuhumar da Hukumar Amsar Korafe-Korafe da yaki da cin Hanci da Rashawa ke yi ma Sarki Sunusi na II, na yin Wadaka da dukiyar Masarauta Har Miliyan Dubu Hudu ba Bisa Ka’ida ba, Jaridar Dimokuradiyya ta Dukufa domin Bayyana Muku Gaskiyar Abin da ke tafiya.
Wakilinmu Baban Khausar Imam, ya Zanta da shugaban Hukumar Barista Muhuyi Magaji, inda ya ce, Mu an Kawo mana Rubutaccen Korafi ne daga cikin Gidan Sarautar Kano, inda Masu korafi suka nemi mu Shiga cikin Lamarin domin a Samu Adalci a Masarautar.
Kadan daga Abin da Korafin ya Kunsa shine, Masarauta tana Wadaka da Walkajami da Asusun Masarautar ba Bisa Ka’ida ba kuma ga Hujjojin su Bayan mun Dauki dogon lokaci muna Nazarin Hujjojin da suka ba mu sai muka ga lallai Akwai kanshin Gaskiya.
Wannan Yasa muka Dubi Sashe na 4 na Kundin Tsarin Tafiyar da Masarauta da Yadda ake Kashe kudade a Masarauta, Bayan nan sai Muka fara Gayyatar wadanda abin ya shafa.
Wadanda suka halarci Kiran da muka yi musu sun ba da Jawabin su a Rubuce Iya Gwargwadon Abin da suka sani wasu kuma suka Ce ba za su samu zuwa ba amma duk abin da za a tambaye su a Shirye suke da su ba da Amsa.
Mutum Hudu kuma daga Cikin su suka ki Amsa Kiranmu kuma suka ki Ba da Uzuri, Tsawon Lokaci Muna Tura Musu da Tuni, amma Suka Share Waje suka yi Zaman suka ce An ki Zuwa din ba za a zo ba.
Wannan Yasa muka dubi Dokokin da suka kafa Wannan Hukuma ta mu inda Muka Nemi Izinin Kotun Majistare Madaukaiya, kan cewa ta bamu dama mu kamo wadannan Mutane da suka ki Amsa Gayyatar mu Haka Siddan.
Domin cikin Binkicen da muka yi mun Gano wasu Lambobin Wayar Tafi da Gidanka na Iyalan Sarki Sunusi na II, da aka rika tura musu katin Waya na Ba gaira babu dalili amma aka sanya Kudin cikin Jerin Kudin da aka Kashe domin yin hidimar Masarauta har Naira Miliyan Ashirin da Tara.
Ku Biyo mu Za mu Cigaba Gobe, don jin Yadda aka kashe Sauran Naira Biliyan Hudun.