Nijeriya ta sake gano masu cutar korona 438 a ranar Asabar, abin da ya sa yawan mutanen da annobar ta kama zuwa yanzu a ƙasar 39,977.
Cibiyar da ke lura da dakile cututtuka masu yaduwa ta Nijeriya, NCDC ita ce ta wallafa hakan a shafinta na Twitter a daren ranar Asabar.
NCDC sun bayyana rashin jindadinsu bisa yadda mutum 11 suka mutu sakamakon cutar a fadin kasar.
A cewarsu, cikin mutum 39,977 da suke dauke da cutar, an sallami mutum 16,948, yayin da 856 suka mutu a fadin jihohi 36 cikin harda birnin tarayya Abuja. al Territory.
NCDC ta ce an samu sabbin masu dauke da cutar ne a jihohi 24 na kasar, inda Legas (123), Kaduna (50), Rivers (40), Edo (37), Adamawa (25), Oyo (20), Nasarawa (16), Osun (15), Enugu (15), FCT (14), Ekiti (13), Ondo (13), Ebonyi (11), Katsina (10), Abia (9), Delta (8), Kwara (4), Ogun (3), Cross River (3), Kano State (3), Bauchi (3), Yobe (2), Sokoto (1) da kuma Neja (1).
NCDC sun sake kira ga ‘yan Nijeriya da su ci gaba dabin matakan kariya daga cutar. Inda suka tabbatar da cewa yanzu akwai cibiyoyin gwajin cutar 59 a fadin Nijeriya.