Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya ziyarci Sanata Ibrahim Shekarau a gidansa dake Mundubawa a daren yau.
Ziyarar da Gwamnan ya kai na zuwane bayan zaizayar magoya baya da jam’iyyar APC ke fuskanta a jihar Kano.
Wata majiya daga fadar Mundubawa ta shaidawa Dimokuraɗiyya cewar galibin magoya bayan Sanata Shekarau dake gidansa yayin da Ganduje ya iso basuji daɗin ziyarar gwamnan na Kano ba.
Yanzu dai ana jiran mataki na gaba da Sanata Shekarau zai dauka, inda ake raɗe-raɗin zai koma jam’iyyaar NNPP.
Sanata Shekarau dai shine ke jagorantar wani bangaren na Jam’iyyar APC a jihar Kano da akewa lakabi da G7, wanda kuma tsagi ne dake adawa da bangaren Gwamna Abdullahi Ganduje.
Kuma tuni wasu daga cikin Mambobin a tsagin G7 din suka kammala shiryawa domin ficewa daga jam’iyyar, bayan da suke ganin baza su samu yancin da suke fata ba a siyasance.