Tsohon mai baiwa shugaban kasa Muhammadu shawara wato Sha’aban Ibrahim Sharada, ya kaddamar da takararsa ta gwamnan Kano a zaben 2023.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Sha’aban Sharada shine dan majalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar birnin yanzu haka.
Taron kaddamar da takarar tasa ya gudana a cibiyar horas da matasa ta Sani Abacha Youth Center dake Karamar hukumar Kumbotso.
KARANTA ANAN: Yajin Aikin ASUU: FG Ta Jaddada Ci Gaba Da Tafiya Kan Tsarin Babu Aiki Babu Biya
Sha’aban Sharada dai ya tsaya takarar fitar da gwani a zaben fidda gwani da aka gudanar, amma kuma ya sha kayi, wannan ya sanya shi ficewa daga jam’iyyar APCn zuwa jam’iyyar ADP.
An dai kai ruwana kan batun takararsa ta gwamna a jamiyyar ADP, tsakaninsa da Haruna Koguna, wanda ya samu tikitin takarar a zaben fidda gwanin jam’iyyar.
A wani labarin kuma: Ban Taba Cewa Wike Ba Uban ‘ya’yansa Bane – Shugaban PDP Ayu
Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu ya musanta cewa ya raina gwamna Nyesom Wike.
A wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar din nan, tsohon shugaban majalisar dattawan ya nisanta kansa daga wasu shafukan sada zumunta da suka yi ta ambato shi yana wulakanta shugaban Ribas.