Shekara tara ke nan a jere, shahararen dan kasuwarnan, Aliko Dangote ana ayyana shi a matsayin wanda ya fi kowa kudi a Afrika baki daya da zunzurutun kudin da ya kai Dala Biliyan 10.1.
A rahotan baya-bayan nan da aka saki na da Jaridar Forbes ta saki na masu kudin duniya, ta bayyana cewa kudin Dangote ya kai Dala Biliyan 10, wanda hakan ke nuna cewa kudinsa ya ragu wanda hakan ya faru sakamakon faduwar darajar kamfanin Simintinsa.
Nahiyar Afrika dai na da kasashe 54, sai dai a cewar Forbes mutum takwas ne kawai za a iya kiran su suna da biliyoyin Daloli, ciki kuwa harda kasashen Afrika ta Kudu da Misra, inda dukkanin mutum 10 na farko da suka fi kowa kudi a Afrika suka fito daga wadannan kasashen.
Inda kuma Nijeriya ke da mutum hudu ciki kuwa harda Aliko Dangote wanda aka ayyana a matsayin wanda ya fi kowa kudi a Afrika.