Wani Likitan yara mai suna Ovo Ogbinaka da ke aiki a garin Benin na jihar Edo ya ce yawaita shan ruwan sanyi na cutar da kiwon lafiyar mutum. Likitan ya ce ya gano hakan ne a binciken da ya yi game shan ruwan sanyi da illar da ke tattare da shi inda sakamakon binciken ya nuna cewa yawan shan ruwan sanyi na sa mutum na haddasa kamuwa da cututtukan dake kama hakarkari da zuciya wanda mutum baya ganewa sai ya fara tsufa.
Illolin da shan ruwan sanyi ko ruwan kankara ke yi sun hada da:
1. Shan ruwan sanyi ko ruwan kankara na sa mutum tsufa da wuri
2. Shan ruwan sanyi ko ruwa mai kankara na kawo mura,tari da toshewar murya.
3. Ya hana narkar da abinci a cikin mutum.
4. Yana daskarar da jijiyoyin jiki wanda hakan ke hana jini gudana.
5. Yana haddasa taruwan kitse a kodar mutum.
6. Yana kuma lalata hanji da hakan ke sa a kamu da ciwon daji.
7. Shan ruwan sanyi na sa kirji ya yi ta ciwo.
8. Shan ruwan sanyi ko ruwa mai kankara na sa mace ta haifi ‘da mai dauke da cutar “pneumonia”