Daga Fulani Shuaibu
Mai karatu dole sai kayi hakuri kan wannan nazarin da nayi game da batun mata da yarjejeniyar Aure a tsakani, dole idan aka taba masoyin ka babu chakka sai kaji ba daidai ba koda kuwa babu yawa.
Anya Iyaye basa bayar da muhimmiyar Gudunmawa wajen sake-saken Aure da wargajewar hadin kan Yara a tsakanin gidajen Iyaye.
Zan dora alkalami na a kan Jarumin masanaantar shirya fina finan Hausa wato Kannywood, Jarumi Adam A Zango Wanda zai yi Aure a Jihar Kebbi karshe makon nan da muke a ciki, Kuma Auren shine karo na shida daga shekarar 2006 zuwa yau 2019.
Tayaya mutun zai dunga Auren Yaran mutane Kuma Yara masu kananan Shekaru amma ya dunga sallamar su kamar Awaki, amma Iyayen mu har yanzu sun kasa hukunta shi.
Shin ya dace Iyayen mu su dunga daukar Ya’yan da suka haifa da cikin su suna bayar da su ga mazaje kawai saboda suna so Ya’yan su suyi Aure da wuri?
Wai dama ba wajibi bane Iyaye su dunga bincikar Mazajen da Ya’yan su zasu Aura saboda samar musu Mazaje na gari masu kishin su dana Ya’yan su?
Lallai Iyayen safiyya dake Kebbi ya kamata ku binciki Jarumi Adam A Zango kafin ranar Daurin Aure gudun kada ku saka Yarinyar ku a halin ha’ula’i.
Yaran sa shida Iyayen su daban daban ina amfanin wannan, shin Ya’yan Jarumin zasu iya samun hadin kai a tsakanin Yan’uwan su, ina taya gida kai a rarrabe.
Abun da Al’umma da Kuma Iyayen Safiyya zasu duba shin yaya aka yi Adam A Zango yake sallamar matayen daya Aura? Shin mene ne dalilin daya saka baya iya rike mata? Shin ya dace a baiwa Wanda yayi Aure karo biyar a tsakanin shekaru 13 mata ya Aura? Tayaya zaayi ace duk cikin Matan daya Aura babu ta kirki?
Ina mai baiwa masu karatu na hakuri lallai wadannan batutuwan abun dubawa ne koda kuwa bazaa fahimce ni ba.