Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na ci gaba da jagorantar taron Majalisar Zartaswar Tarayya karo na arba’in da biyu ta na’ura.
Daga mahalarta taron akwai Mataimakin Shugaban Kasa Farfesa Yemi Osinbajo da Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha gami da shugaban ma’aikatan fadar gwamnati Ibrahim Gambari.
Kazalika akwai ministoci shida dake halartar taron da suka hada da na yada labarai Lai Muhammad da Ministar Kudi Zainab Ahmad da na Shari’a Abubakar Malami gami da Ministan harkokin cikin gida Rauf Aregbesola.
Sauran sun hada da Ministan birnin tarayya Abuja Muhammad Bello da kuma na ayyuka da gidaje Babatunde Fashola.
Yayin da shi kuma shugaban ma’aikatan Gwamnatin Tarayya Folasade Yemi-Esan da Ministoci dake halartar taron mako na mukarabban gwamnati ko wannen su a ofishin sa dakw Abuja