Shugaban kasa Muhammadu Buhari a jiya Litinin ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Borno bisa rasuwar tsohon ministan ma’adinai, wutar lantarki da karafa, Bunu Sheriff Musa.
Shugaban, a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Femi Adesina, ya fitar, ya bayyana alhinin da ‘yan uwa suka yi na rashin marigayin.
Ya kuma jajanta wa kungiyar dattawan jihar Borno, abokai da abokan tsohon ministan, wadanda suka yi aiki daban-daban a matsayin Ministan Masana’antu a shekarar (1985), Ma’adinai, Wutar Lantarki da Karfe (1986-89), Jirgin Sama (1989), Albarkatun Ruwa (1990). da dai sauran su.
Buhari ya ce marigayin ya bayar da gudunmawa wajen ci gaban kasa da al’ummarsa ta hanyar daukar wasu ayyuka da dama ciki har da Jakadan Najeriya a Faransa.
Buhari, wanda ya yi addu’ar Allah ya jikan sa, ya bukaci ‘yan uwansa da su karbi ta’aziyyarsa cikin jerin ga na sauran mutane.