Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja a ranar Juma’a zuwa Daura dake jiharsa ta haihuwa Katsina, domin yin rijistar jam’iyya da kuma sabunta zamansa mamba a jam’iyyar ta APC.
Kamfanin dillancin lbarai na kasar NAN ya ruwaito cewa shugaban kasar ya bar Abuja ne bayan idar da sallar Juma’a a masallacin fadar gwamnati.
A ranar Asabar ake sa ran shugaban zai je mazabar Sarkin Yara a Daura, domin sabunta katinsa na dan jam’iyyar APC da misalin karfe 12 na rana.
A ranar Alhamis ne daraktan jam’iyyar Farfesa Ussifu Medaner ya ce babu wakilci a aikin sabunta zama dan jam’iyyar.
Ya ce wannan aiki na da matukar mahimmanci kuma akwai wasu abubuwa na daban da yake da su wadanda za a fuskanta a zabuka nan gaba.
Medaner ya ce akwai bukatar kowa ya je da kansa domin yin wannan rijista, yana jaddada cewa ba za su amince da wakilci ba.