Daga: Abbas Yakubu Yaura
Mukaddashin rundunar FRSC, Dauda Ali Biu, ya ba da kwakkwaran umarni ga kwamandojin sassan 37 da su fara aiki nan take, tare da aiwatar da cikakken karfin doka kan duk wasu babur da aka gani ba tare da rajistar da ta dace ba.
Biu ya nuna damuwarsa kan yadda baburan da ke bin hanyoyin ke kara tabarbarewa kuma akwai bukatar a tabbatar da cewa an kama dukkan babura masu kafa biyu yadda ya kamata a cikin kundin tsarin tantance ababen hawa na kasa.
Kakakin hukumar FRSC, Mista Bisi Kazeem a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin din da ta gabata ya ce umarnin ya zo ne biyo bayan bukatar da gwamnatin tarayya ta bayar na dakile gungun miyagu babura a kan titunan Najeriya.
KARANTA WANNAN LABARIN: 2023: INEC Ta Bukaci NASS Ta Zartar Da Dokar Aikata Laifukan Zabe
Ya kara da cewa rashin tsaro ne ya sanya hakan ya zama dole a kawo karshen ayyukan wadannan nau’ukan babura ba tare da yin rajista a kan tituna ba.
A yayin da ya ke bayar da muhimmanci musamman kan illolin tsaro na rashin kame duk wasu babura da ke cikin ma’ajiyar bayanai ta kasa, Mukaddashin Rundunar ta FRSC ya bukaci kwamandojin sashen da su gaggauta yin hulda da hukumar tattara kudaden shiga a jihohinsu, tare da kafa wata Task Force tare da hadin gwiwar ‘yan sandan Najeriya da sauran hukumomin tsaro a inda ya dace, ciki har da ofishin duba ababen hawa da sauran masu ruwa da tsaki don aiwatar da ingantaccen aiki.
“Da fatan dai, umarnin ya kuma nuna cewa za a kama baburan da ba su yi rajista ba yayin da aka ba su umarnin su fara tare da kammala cikakken rajistar baburan kafin a sako su.
“Mukaddashin rundunar Marshal ya ce an gudanar da aikin ne domin a yi wa baburan rajista da kuma rubuta su a cikin ma’adanar bayanai ta kasa. Don haka, masu aiki bazai bayar da sanarwar tikitin laifi ga masu aiki ba.
“Duk da haka, duk babur da aka kama dole ne a rubuta cikakken bayani,” in ji Kazeem.