Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da watan Fabrairu 2022 domin gudanar da babban taron jam’iyyar (APC) na kasa.
Shugaban kungiyar gwamnonin Jam’iyyar APC kuma gwamnan jihar Kebbi, Atiku Bagudu ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Abuja.
Ya bayyanawa manema labarai na fadar shugaban kasa bayan ganawarsa da shugaban kasar a fadar shugaban kasa dake babban birnin kasar.
Gwamna Bagudu ya samu rakiyar shugaban kwamitin riko na jam’iyyar APC na kasa kuma gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, da kuma gwamna Abubakar Badaru na jihar Jigawa.
Ya shaida wa manema labarai na fadar gwamnati cewa domin bayyanawa shugaban kasa shawarar kungiyar gwamnonin cigaba a lokacin da mambobin suka hadu a daren Lahadi.
A cewar Bagudu, gwamnonin sun yanke shawarar cewa za a gudanar da babban taron a watan Fabrairun 2022 kuma an gabatar da irin wannan shawara ga shugaban kasa don amincewa.
Sai dai ya bayyana cewa har yanzu shugabannin jam’iyyar ba su yanke shawara kan takamaiman ranar da za a gudanar da babban taron nata na kasa ba.
Gwamnan ya ce jam’iyyar za ta sanar da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) yayin da ta fitar da jadawalin.
Jaridar Dimukuradiyya ta rawaito cewa Gwamna Buni ya karbi ragamar shugabancin jam’iyyar APC ne a watan Yunin 2020 bayan rusa kwamitin gudanarwa na jam’iyyar (NWC) karkashin jagorancin tsohon gwamnan jihar Edo, Adams Oshiomhole.
A cikin rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar a matakin kasa a wancan lokacin, majalisar zartaswar jam’iyyar APC ta kasa ta yi taro inda ta yanke shawarar rusa jam’iyyar NWC bisa shawarar da shugaban kasa ya bayar.