Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kaddamar da cibiyar kula da masu cutar daji wato kansa a Kano ta biliyoyin naira kafin karshen Oktoba, 2022.
Kwamishinan lafiya na jihar, Dr. Aminu Ibrahim Tsanyawa wanda a ranar Lahadin nan ya bayyana cewa tuni an kusa kammala ginin cibiyar kula da lafiyar ta duniya da gwamnatin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ke ginawa.
Kwamishinan lafiyar ya yi magana ne a lokacin da yake jawabi ga manema labarai gabanin bikin makon lafiya matakin farko na jihar da aka shirya farawa gobe Litinin.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Dokta Tsanyawa ya bayyana cewa taron na tsawon mako guda an shirya shi ne domin nuna irin nasarorin da gwamnati mai ci ta samu wajen inganta harkokin kiwon lafiya a Kano.
KARANTA KUMA: Gwamnatin Tarayya Ta Ware Biliyan Guda Don Magance Cutar Kansa
Ya tunatar da cewa baya ga jerin abubuwan da aka tsara don tunawa da makon lafiya, bikin zai kuma ba da damar yin la’akari da kalubale da kuma kokarin dinke baraka a fannin na lafiya.
Da yake mayar da martani game da kalubalen da ke tattare da aiwatar da asusun samar da kiwon lafiya na asali a Kano, kwamishinan ya tabbatar da cewa matsalolin da ake fuskanta a halin yanzu suna da matukar wahala a aiwatar da shirin.
Sai dai ya yi nuni da cewa, hukumomin biyu, hukumar kula da lafiya matakin farko ta jiha da kuma tsarin bayar da gudunmawar inshorar lafiya na jiha, da ke kula da aiwatar da asusun suna aiki tukuru domin gyara matsalolin.
Jaridar Solacebace ta rawaito cewa, Wani bangare na ayyukan da aka zayyana a makon lafiya sun hada da rarraba wasikun nadin sabbin ma’aikatan lafiya da aka dauka aiki, kaddamar da babban asibitin Rano, gudanar da aikin jinya a masarautar Rano da kuma makon shayar da nono ta shekarar 2022.
Sauran jerin abubuwan da zasu faru sun hada da rarraba kayayyakin haihuwa kyauta, kaddamar da allurar Rota, kaddamar da ranar kare lafiyar marasa lafiya ta duniya, kaddamar da wasu zababbun cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 30 da aka gyara ta hanyar ceton rayuka miliyan daya da sauran ayyuka.
A wani labarin kuma: 2023: Tinubu Ya Nada Yahaya Bello Ko’odinetan Matasa Na Kasa
An nada Gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi a matsayin ko’odinetan matasa na kwamitin yakin neman zaben Tinubu da Shettima na kasa.
An mika nadin ne a wata wasika da aka aike wa Gwamna Bello mai dauke da sa hannun dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu.