’Yan bindiga sun yi garkuwa da Shugaba da kuma Sakataren Kungiyar Malaman Manyan Kwalejin Fasaha ta Oyo da ke Igbo-Ora. An sace Opadijo Olujide tare da wasu mutum hudu kamar yadda Rundunar ’Yan Sandan Jihar Oyo tabbatar.
Malamin ya na koyarwa ne a Kwalejin noma da fasaha dake jihar Oyo. Sannan bayanai sun tabbatar da cewa; an samu labarin cewa Olujide da shi Sakataren Kungiyar, Gbenga Alayande da wasu mutum uku duk an sace su a kan hanyar su ta dawowa daga wani taron da suka halarta a garin Saki a ranar Alhamis.
Sai dai an tabbatar da cewa; hukumar kwalejin na ta kokarin ganin an sako su. Su kuma ‘yan sanda na biye da al’amarin.
Kakakin Yada Labarai na ‘Yan Sandan Jihar, Olugbenga Fadeyi, wanda ya tabbatar da yin garkuwa da Malaman, ya ce jami’an su na ci gaba da binciken al’amarin.