Shugaban majalisar Dattawan Nijeriya, Ahmad Lawan ya dauki nauyin aurar da mutum 300 a Yobe ta arewa.
Ezrel Tabiowo, mai taimaka masa kan harkokin watsa labarai, shi ne ya bayyana hakan a cikin sanarwar da ya fitar a ranar Asabar a Abuja.
Ezrel ya ce wadanda suka amfana daga wannan tallafin na Sanatan sun fito ne daga kananan hukumomi shida da suke karkashin mazabarsa da suka hada da Barde, Jakusko, Machina, Yusufari, Nguru da Karasuwa.
Ya tabbatar da cewa wadanda Sanatan ya tallafawa sune wadanda suka shirya yin aure kuma sun kai shekarun auren, amma kuma ba su da wadanda za su tallafa musu a yi auren. A cewarsa, ya dauki nauyin auren ne bayan da ya samu korafin bukatar hakan daga iyayen a lokacin da ya ziyarci mazabarsa ta Yobe ta arewa.
“An gudanar da auren ne a matakai uku ta hanyar bin dokokin kariya daga cutar korona, wanda aka fara shi daga ranar Asabar.” Ya tabbatar.
Ya kara da cewa; a mataki na farko, an aurar da ma’aurata 100 ne, wadanda aka zabo daga kananan hukumomin Barde da Jakusko a jihar ta Yobe. “An yi auren ne a masarautar Barde a ranar Asabar, inda aka daura wa masu niyyar auren kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a babban Masallacin Barde.” Inji sanarwar.
“Sai kuma mutum 100 daga kananan hukumomin Nguru da Karasuwa da ake sa ran za a yi musu aure a mataki na biyu.” Inji sanarwar.
Ya kara da cewa; “Sai sauran 100 din daga kananan hukumomin Machina da Yusufari a mataki na uku.” Ya tabbatar.
Sanarwar ta tabbatar da cewa mutum 100 din da aka yi wa auren, Sanata Ahmad Lawan wanda yake shi ne Sardaunan masarautar Bade, ya biya kudin sadakinsu. Ya kuma tabbatar da cewa Sanatan ya dauki nauyin dukkanin kayayyakin dakin ma’auratan da suka fito daga gunduma 60 daga kananan hukumomi shida na yankin Sanatan.