Shugaban Sojojin Najeriya ya Ziyarci Shehun Borno
Shugaban Sojojin Najeriya Faruk Yahaya yace Sarkunan Gargajiya nada matukar muhimmanci wajan kawo karshen rikici dake faruwa Arewa.
Shugaban Sojojin Najeriya Faruk Yahaya ya bayyana hakane lokacin da ya kaima Sarkin Borno Ziyara Alhaji Abubakar Ibn Umar Garbai El-Kanemi, da kuma sauran mabiyan sa a fadar sa dake garin Borno a ranar Juma’a 25 ga watan Yuni.
KARANTA:-Gwamnatin Jahar Kwara Zata Gina Katafaren Asibitin Maganin Ciwon Daji
Kamar yadda kwanel Ado Isah ya bayyana yace Shugaban Sojojin Najeriya Faruk Yahaya yayi matukar farin ciki da ziyartar Sarkin Borno.
Shugaban Sojojin Najeriya Faruk Yahaya yace naji dadi dana kawo ma Shehun Borno Ziyara a matsayin sa na Baba, Kuma shugaba ba a Borno kadai ba a gaba daya ilahirin Kasar, sannan Faruk Yahaya ya sami albarka don cimma nasara akan aikin dake tunkarar sa.
Shugaban Sojojin Najeriya yace yayi farin ciki sosai da irin kulawa sa Masarautar take tun yana Jagorantar rundunar HADIN KAI kamin a bashi mukamin Shugaban Sojojin Najeriya na 22.
Mai girma Shehun Borno ya yabama sojojin Najeriya kan irin kokarin da sukeyi kan zaman Lafiya ya tabbata a Arewa.
Yace Kananan Hukumomi 17 daga 27 duk suna mallakin Yan bokoharam ne amma yanzu duk Mutane sun dawo cikinsu.
A Ziyarar Shugaban Sojojin akwai Manjo Janar Ibrahim Yusuf, da kuma wasu manya-manyan sojoji har da Jagoran Rundunar HADIN KAI.
Comments 1