Mukaddashin shugaban jam’iyar PDP na Kasa Yemi Akinwonmi a jiya Talata, ya jagoranci tawagar Shuwagabannin jam’iyar, domin ziyarar Tsohon Shugaban kasa Goodluck Jonathan a gidan shi dake babban birnin tarayya Abuja.
Wadanda shuka raka Akinwonmi sun hada da tsohon sakataran ruko na jam:Iyar a yankin Kudu maso Yammacin kasar nan Daisi Akintan, da kuma daya daga cikin mambobin kwamitin zartarwar jam’iyar Mrs Helen Taiwo.
Dukkannin su uku, sun gana da Tsohon Shugaban kasa ne a sirirran ce, da ake kyautata zaton cewa, sun na bukatar Jonathan ne da ya ci gaba da zama a Jam’iyar PDP, tare da basu ingantacciyar shawara da za ta taimaka wajan magance rikice-rikicen da suka dabai-baye jam’iyar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Kwalara ta kashe mutum 43, mutane 559 sun kamu a Borno
Wata majiya da ke da masaniya game da taron ta ce, “Tawagar jam’iyar na shiyar Kudu maso Yammacin kasar nan, sun gana da tsohon Shugaban kasar ne, don rokon sa, da kada ya fice daga jam’iyyar.”
“Sun Kuma bukace shi, da nuna damuwar shi da jam’iyar, ta hanyan shiga al’amuranta na yau da kullun, inda shi ma Tsohon Shugaban kasar, ya bai wa tawagar tabbacin cewa, bazai fice daga jam’iyar ba” a cewar majiyar.
A wani labarin Kuma na daban.
Yan bindiga sun yi garkuwa da akalla Mabiya cocin darikar Living Faith, da a kafi sani da Winner Chapel, dake yanki Osara na karamar hukumar Adavi a jihar Kogi.
A cewar rahoton yan bindiga sun afka cocin ne da yawan gaske, ya yin da Mabiya mambobin cocin ke wani bita a karshen makon daya gabata.
Maharan sun sun fara harbi kan me uwa da wabi a kusa da Majami’ar, domin tsoratar wa kafin daga bisani su yi awangaba da Mambobin cocin zuwa wani wuri da ba’asan ko inane ba.
Lokacin da ya ke tabbatar da kai harin ga manema labarai, Shugaban karamar hukumar Adavi na jihar Kogi Joseph Omuya Salami, ta bakin Babban Mai bashi shawara akan kafafen yada labarai Habeeb Jamiu ya ce, yan bindigan sun ta yin harbe-harbe a iska domin tsoratar da al’umar yankin, kafin su tafi da wadanda su ka yi garkuwa da su.
A cewar Jamiu, Shugaban karamar hukumar ya ziyarci inda lamarin ya afku, tare da Jami’in dansandan dake kula da yankin na Osara
Kazalika Habeeb Jamiu ya Kara da cewa, Karamar hukumar na tattauna wa da hukumomin tsaron yankin, domin tabbatar da an kubutar da wadanda aka sace lami lafiya.
Sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan jihar Kogi CSP Williams Ovye Aya, bai dauki wayar salula ba kafin hada wannan rahoton.