Babban Sifeton ‘yan sanda, IGP Usman Baba, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan ƙawanyar da wasu jami’an tsaro suka yiwa gidan mai shari’a Mary Odili ta Kotun Koli dake Abuja.
A ranar Juma’a, 29 ga watan Oktoba, 2021, jami’an tsaro da ake zargin ‘yan Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Tu’annati (EFCC) da kuma Hukumar Tsaro ta farin kaya (DSS), suka kai wani sumame gidan Mai shari’a Odili da ke Abuja, wanda kuma wannan mataki da suka dauka ya jawo Allah wadai daga bangarori da dama.
Bayan mamayar dai, EFCC da DSS sun musanta hannu a wannan atisayen da bai yi nasara ba, wanda ya janyo tofin Allah tsine.
Mai magana da yawun rundunar na kasa, CP Frank Mba, ya ce Babban Sifeton rundunar ya lura cewa shugabancin rundunar ba ta da masaniya kuma babu wani lokaci da ya umarci jami’an ‘yan sanda su gudanar da irin wannan aiki.
Alkali, ya bayyana rahoton keta alfarmar gidan mai shari’a. na Kotun Koli a matsayin abin takaici da rashin yarda.
Ya kuma tabbatar da aniyar rundunar na tabbatar da tsaro da tsaron ‘yan majalisar shari’a da ‘yan Najeriya baki daya.
Ya kuma yi kira da a kwantar da hankula, inda ya yi alkawarin cewa rundunar za ta yi duk mai yiwuwa wajen bankado masu aikata wannan aika-aika da kuma dalilan da suka suka aikata hakan, tare da alkawarin gurfanar da duk wadanda ake tuhuma a gaban kotu.