Rundunar soji ta Operation Sahel Sanity ta cafke mutum 150 da zargin fashin daji a wani simame da ta kai wani wurin haƙar ma’adanai.
Babban jami’in sadarwa na rundunar, Birgediya Benard Onyeuko, sanarwar da ya fitar a ranar Talata ya ce ’yan dabar dajin da aka ƙwace ƙananan bindigogin hannu 20 a wurinsu na amfani da wurin a matsayin mafaka.
Ya ce an mahaƙar ma’adinan da aka kama mutanen na yankin Gadan Zaima na ƙaramar hukumar Bukkuyum a jihar Zamfara.
Haka kuma a sintirin da dakaru suka saba gudanarwa, sun yi arangama da ‘yan bindiga uku a kan babura a kusa da ƙauyen Maigama na ƙaramar hukumar Anka suna shirin kai wa mazauna ƙauyen hari.
https://dimokuradiyya.com.ng/yan-bindiga-sun-sace-shanu-500-a-zamfara/
A yayin artabu, sojojin sun kashe ɗan ta’adda ɗaya, yayin da ragowar biyun suka arce da kafafunsu tare da zubar ba makamansu ciki har da bindigogi kirar AK-47 da kuma alburusai da dama.
Birgediya Benard ya kara da cewa, wani jagoran ‘yan daban daji mai suna Bornon Kejo, ya mika wuya ga dakaru a Karamar Hukumar Zurmi ta Jihar, ya kuma ajiye makamansa na yaki da suka haɗar da bindigogi biyu ƙirar Ak-47 da alburusai.
Sojoji sun kuma datse wasu motoci bakwai maƙare da shanu a babbar hanyar Jibiya zuwa Katsina da kuma hanya Gusau zuwa Zariya wanda ake zargin na sata ne.
A yanzu haka dai an miƙa shanun a hannu rundunar ‘yan sanda ta jihar Katsina domin ɗaukar matakin da ya dace.