Dakarun Sojin Najeriya sun damke shugaban wata kungiyar ‘yan bindiga mai suna Shehu Jatau, tare da yaransa biyar a wani Otal a kwaryar birnin tarayya Abuja. Jatau da ‘yan kungiyarsa ne suka addabi birnin tarayya da fashi da kuma garkuwa da mutane.
A ranar Asabar, hukumar Sojin ta bayyana cewa binciken da aka fara kaddamarwa ya nuna cewa sun kasance masu tayar da zaune tsaye a jihar Filato amma suka koma Abuja domin garkuwa da mutane da fashi.
Jami’in yada labarai na hukumar Soji, Kanal Aminu Iliyasu, a jawabin da ya saki ya tabbatar da damke su. Iliyasu ya kara da cewa: “Wani kasurgumin shugaban ‘yan bindigan kabilar Tarok, Shehu Jatau, tare da abokan aikinsa biyar sun shiga hannu a sintirin da aka kai musu cikin dakin Otal cikin garin Abuja.” In ji shi.
Ya ci gaba da cewa; bincike ya nuna cewa ‘yan bindigar sun kasance masu tayar da tarzoma a jihar Filato da aka yi asarar rayuka da dukiyoyin biliyoyin Naira.
A cewarrsa; “Amma da aka samu zaman lafiya a jihar, sai suka koma garkuwa da mutane, sace-sace da kaiwa mutane hari.”