A ranar Alhamis ne rundunar sojojin Nijeriya suka fatattaki wadansu ‘yan bindiga da suka far wa gonar tsohon gwamnan jihar Zamfara Ahmad Yarima. A yayin arangamar da suka yi dakarun Sojin sun kashe ‘yan bindiga sama da 100 inda sojoji biyar ne suka rasa rayuwarsu a inda kuma wadansu guda 4 suka jikkata.
Wannan tashin hankalin ya auku ne a karamar hukumar Bakura dake jihar Zamfara inda a nan ne gonar yake.
Wadansu mazauna karamar hukumar sun bayyana cewa akalla ‘yan bindiga 200 dauke da bindigogi ne suka far wa wannan gona inda suka kashe masu gadin gonar guda biyu nan take.
Kakakin rundunar Atisayen Hadarin Daji a jihar Zamfara, Oni Orisan ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya kara da cewa; har yanzu ana gudanar da bincike a kai.
Idan ba a manta ba a watan Satumba sulhun da Gwamnatin Jihar Zamfara ta yi da ‘yan bindiga masu garkuwa da kai hare-hare, ya sa aka saki mutum 72 da aka yi garkuwa da su.
An kuma samu adadin ‘yan bindiga 240 wadanda suka mika makaman su tare da tuba daga aikata mugayen halaye.