• A safiyar yau a asabar, rundunar soji ta kasa ta ce, ta kashe yan bindiga da dama.
• An kwato Arsashin makami kiran PKT da kuma alburusai da dama a hannun yan bindigan.
• Rundunar soji ta bukaci Al’umar Yankin Arewa maso Gabas da ta cigaba da bata goyan baya domin kamawa da yan bindiga a yankin.
Rundunar soji ta kasa, ta ce jami’an ta na rundunar ta 8, sun yi nasaran kashe yan bindiga da dama, a karamar hukumar Talata Marafa a jihar Zamufara.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar soji ta kasa Onyema Nwachukwu ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa da ya fita a babban birnin tarayya Abuja.
KARANTA WANNAN LABARIN: Masu garkuwa sun bukaci Naira Milliyan 22 da dubu dari 5 amastayin kudin fansan Dali ban Kwalejin Nuhu Bamalli
Birgediya Janar Nwachukwu ya ce, Rundunar ta kai wa yan bindigan farmaki ne a maboyar su, da ke kusa da yankin Mayanchi-Dogo Karfe da Kauyen Fagantama da ke jihar Zamfara.
A cewar sa, rundunar ta kuma kwace Arsashin makami kiran PKT, da tarin alburusain bindiga, da kuma mashin.
A karshe ya bukaci Al’umar yankin Arewa maso Gabashin kasar nan, da su cigaba da bai wa jami’an tsaro goyan baya a kowani lokaci, domin kakkabe yan bindiga a yankin” inji shi.