By Abbas Yakubu Yaura
Jami’an tsaro sun kashe ‘yan bindiga da dama tare da lalata sansanonin su a yayin wani aikin share fage a kananan hukumomin Igabi da Chikun na jihar Kaduna.
Sojojin sun kuma kama wani Malam Idris Audu, wanda shine malamin tsubbun ‘yan bindigar da wata mata mai suna Rabi Hajiya Karime, wadda aka ce itace matar wani sannanen dan bindiga ce mai suna Zubairu.
Kwamishinan tsaron da harkokin cikin gida na jihar Kaduna, Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.Ya kara da cewa jami’an tsaro sun kama wani Abdulrasheed Gambo Na Halima da Abubakar Idris Na Halima a matsayin wadanda ake zargi da hada baki dasu.
Aruwan ya ce an gudanar da aikin share fage ne a Faka, Katuka, Barebari da Maguzawa.sannan ya yi nuni da cewa an ga wasu ‘yan bindiga da ba a tabbatar da adadinsu ba a kan tudu da ke tsallaken kogin Maguzawa, inda ya kara da cewa, “An kama su ne da wani jirgin sama mai saukar ungulu na rundunar sojojin saman Najeriya, inda suka kashe su.
Ya ce jami’an tsaron sun gudanar da sintiri daidai wa daida zuwa Katuka mai tazarar kilomita 9 daga Kangon Kadi a karamar hukumar Chikun, inda aka kama wani dan bindiga da ya gudu.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Aruwan yace an kwato wasu babura, bindiga kirar AK 47 guda daya, wasu harsasai na AK 47, alburusai da kuma kwayoyi bayan sun fatattaki wasu sansanonin ‘yan bindiga a Udawa dake Chikun.