Sojoji a jihar Benuwe sun kashe ƙasurgumin ɗan ta’addan da ake nema ruwa a jallo Terwase Akwaza.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa, kwamandan rundunar sojin ta musamman Manjo Janar Moundhey Ali, ya ce an kashe Gana ne a wani sumamen bincike na sojoji a kan hanyar Gbese-Gboko-Makurdi, bayan musayar wuta wuta da ’yan bindiga.
“Bayan samu bayanan sirri game da tafiya Terwase Akwazwa Agabu a kan hanyar Gbese-Gboko-Makurdi.
“Nan take dakarun rundunar sojin ‘Ayem Akpatuma III suka fara bincike a kan hanyar.
“Da misalin ƙarfe ɗaya na rana aka yi arangama da tawagar Gana, inda aka yi musayar wutar aka kuma kashe shi”, cewar Janar Ali.
Kwamandan ya ce sojoji sun kuma yi nasarar cafke 40 daga cikin yaran Gana a lokacin artabun, kuma za su miƙa su a hannun hukumomin da suka dace domin zurfafa bincike a kansu.
Janar Ali ya ce an ƙwace manyan bindigogi iri-iri da albarusai da ababen fashewa daga hannun ’yan ta’addan.
Ya kuma ƙara da cewa gawar Gana na ajiye a wani asibiti da ba zasu bayyana sunansa ba.