By Abbas Yakubu Yaura
Dakarun hadin gwiwa na kasa da kasa (MNJTF) sun kawar da mayakan Boko Haram da ISWAP 300 a tafkin Chadi.
Laftanal Kanal Kamarudeen Adegoke, babban jami’in yada labarai na rundunar ya fitar da sanarwa a ranar Asabar.
Kakakin ya ce an kashe ‘yan ta’addar ne a cikin arangama daban-daban guda 30.
Kwamandan rundunar, Janar Abdul Khalifa ya yi magana a wani taro da dukkan kwamandojin na MNJTF.
Khalifa ya ce an lura da karuwar amfani da na’urori masu fashewa (IED) da maharan ke yi, kuma an dauki matakan da suka dace dan kawar dasu.
“Kimanin masana’antun sarrafa bama-bamai guda hudu ne aka lalata a yayin gudanar da ayyukan ya zuwa yanzu”, in ji Janar din.
An yabawa Rundunar Sojojin MNJTF/Operation Hadin Kai bisa gagarumin rawar da suka taka.
Jiragen yakin sun lalata sansanonin abokan gaba da dama da kayan aiki da kwamandoji.
Na baya-bayan nan shi ne Abu Ibrahim, shugaban ISWAP da aka halaka a tafkin Chadi Tunbumas.
Khalifa ya kara da cewa sama da ‘yan ta’adda 52,000 da suka hada da mayaka, wadanda aka tura da karfi da kuma iyalansu da suka mika wuya.
Comments 1