Gwamnatin kasar Sudan ta mika wasu membobin kungiyar ‘Muslim Brotherhood’ ga gwamnatin kasar Masar bayan da ta kame su a cikin kasarta.
Tashar Russia Today ta bayar da rahoton cewa, jami’an tsaron kasar Sudan sun mika wasu daga cikin ‘yan kungiyar Muslim Brotherhood ‘yan kasar Masar da suke zaune a cikin Sudan bayan kame su, tare da mika su ga gwamnatin kasar ta Masar.
Jaridar Al-ittihad ta kasar UAE ta rubuta cewa, ‘yan kungiyar Muslim Brotherhood suna kyakkyawar alaka da gwamnatin Sudan a lokacin mulkin hambararren shugaban kasar Omar Albashir, amma bayan da sojoji suka karbi mulki, sun ta kama ‘ya’yan kungiyar suna mika su ga gwamnatin Masar.
Daga cikin wadanda aka mika har da wasu manyan kusoshi biyar na (Sawa’id Misr) bangaren soji na Muslim Brotherhood, wadanda gwamnatin Masar take nemansu ruwa a jallo.
Gwamnatin soji ta Sudan ta bayyana cewa, bayan faduwar Albashir, an kame ‘yan kungiyar Muslim Brotherhood da dama da suka shigo Sudan, suna hankoron zuwa kasar Turkiya.