Kungiyar da ke jagorantar zanga-zanga a Sudan ta amince da shawarwarin da Mahmoud Dardir ya bayar, wanda shi ne mai shiga tsakani ne da ya zo daga Ethiopia, domin ganin cewa an samu sulhu tsakanin sojoji da fararen hula a kasar.
An bayyana cewa mai shiga tsakanin ya bayar da shawarar cewa ko wane bangare tsakanin sojojin da fararen hula ya samu kujeru bakwai- bakwai a majalisar hadaka tsakanin sojoji da farar hula, wacce za ta saka ido kan harkokin gudanarwa na kasar.
Har yanzu dai bangaren sojin na Sudan din ba su ce komai ba dangane da wannan lamari.
Tun bayan hambarar da shugaba Omar al-Bashir ake ci gaba da samun rashin jituwa tsakanin sojojin kasar da kuma farar hula.
A Kwanakin baya ne dai majalisar soji ta mulkin wucin-gadi a Sudan din ta amince cewa ita ta bayar da umarnin tarwatsa masu zanga-zanga a kasar, wanda a yayin hakan aka harbe gwamman mutane.
Kakakin majalisar sojin ya amsa cewa an yi kura-kurai a yayin tarwatsa masu zaman dirshan din a wajen hedikwatar sojin kasar da ke tsakiyar babban birnin kasar ta Sudan, Khartoum.