Hukumar Kwastam ta Najeriya ta fitar da sakamakon karshe na daukar sabbin Jami’an ta na shekarar 2021.
A cewar sanarwar da hukumar ta fitar, ana bukatar wadanda aka lissafa su gabatar da kansu zuwa ofishin Kwanturola, Hukumar Kwastam ta Najeriya, Tsohuwar Sakatariyar Tarayya dake, Area 1, Garki, Abuja daga ranar Litinin 8 ga watan Nuwamban Shekarar nan, zuwa Talata 7 ga watan Disamba, 2021 don tattara bayanan su.
Ana sa ran ‘yan wadanda sukaga sunayen su, za su je Ofishin tare da abubuwa kamar haka kamar haka:
1- Dukkannin Takaddun Karatun su Na Asali
2- Takaddar Shedar Zama Dan Karamar Hukuma
3- Takardun Haihuwa
4- Kwafi hudu (4) kowanne daga cikin takardun su
5- Hotunan fasfo guda hudu (4).
A ƙasa akwai jerin sunayen ‘yan takara masu nasara
Comments 1