A jiya juma’a kungiyar Barcelona ta sanar da cimma yarjejeniya da tsohon tauraron ta Xavi Hernandez a matsayin sabon mai horar da kungiyar Barcalonna bayan da magabatan kungiyar suka sallami Ronald Koeman.
Da samun wannan labari,Xavi Hernadez dake horar da kungiyar Al-Sadd (Qatar), ya bayyana cewa lokaci ya yi na dawowwa gida,yayinda kungiyar ta Barcalona a shafin ta na twitter ta ke yi masa mar’habin.Za a gabatar da sabon kocin ga manema labarai a yau asabar a birnin Catalogne na kasar spain.
Ana hasashen zuwa zai taimaka na sake dawo da kungiyar sahun gaba a gasar la Liga da wasu manyan wasanni na Turai ga baki daya.