Biyo bayan kai hari da ‘yan bindiga suka yi a kauyen Dagwarwa dake karamar hukumar Kurfi dake jihar Katsina yayi sanadiyyar rasa rayukan mutane biyu.
Wata majiya ta shaida mana cewa ‘yan bidingar sun shiga gidan Malam Mu’azu da misalin karfe 1 na dare.
Majiyar ta ce ‘yan bindigar sun kashe yaron Malam Mu’azu da kuma kaninsa, sai dai ba a tabbacin ko sun samu Malam Mu’azu a gida.
Sai dai ba a da tabbacin Malam Mu’azu yana gidan ko kuma ya samu damar tserewa a lokacin da suka kawo farmakin.
Wani mazaunin yankin ya shaida mana cewa, ‘yan bindigar sun yiwa kauyen kawanya ne cikin dare inda suka zo akan babura dauke da muggan makamai.
Ya kara da cewa jama’ar kauyen na cikin firgici sakamakon shigowar ‘yan bindigar, wanda sanadin hakan wasu da yawa sun fara tunanin yin kaura zuwa wani wajen.
https://dimokuradiyya.com.ng/yan-bindiga-sun-kashe-shugaban-jamiyyar-apc-a-katsina/
Gawar wadanda aka kashe za a yi musu jana’iza kamar yadda addini ya tanada.
A cikin kasa da sati guda kenan, ‘Yan bindiga suka shiga karamar hukumar Batsari tare da hallaka shugaban karamar hukumar Abdulhamid Sani.
Har wa yau, ‘Yan bindigar sun sake shiga garin Danmusa inda suka kashe hakimin garin Atiku Maidabino tare da mai gadinsa, duk a kasa da sati daya.
Sakataren gwamnatin jihar Mustapha Inuwa ya tabbatar da cewa zasu yi aiki gagarumi tare da jami’an tsaro domin gano wanda suke aikata wannan mummuna laifuka.
Sai dai ya zuwa yanzu da muke hada wannan labari, an kasa samun kakakin hukumar ‘yan sandan jihar Katsina SP Gambo Isah, domin jin ta bakinsa dangane da wannan labari na karamar hukumar Kurfi.