Kungiyar kiristoci ta kasa CAN ta koka kan yadda Shugaba Muhammad Buhari ya tafi kasar saudiya Dan yin taron hadakar kungiyar musulamai kwana daya bayan rantsar da shi.
CAN wannan na nuni cewa tafiyar bata cikin tsarin dokar kasa tace ta damu matuka kan kokarin Musulantar da kasa.
A wata sanarwa da ta fitar ranar asabar Ta bakin Fasto Adebayo Oladije, mai magana da yawun kungiyar ta CAN da shugaban ta Rabaran Samson Ayokunle, sunyi mamakin yadda shugaban yaje taron inda suke ce suna sa ran zuwan shi taron su na kiristoci ko kuwa ya aika mataimakin shi ya wakilce shi.
CAN tace Buhari ya fara zangon shi na biyu a ofis, ya kamata matsalar tsaro tazo karshe domin ba wanda yasan wadanda zai Nada da basu mukamai a Gwamnatin sa musamman bangaren tsaro.
Sun koka kan yadda ake ta abun da ba tsarin kundin mulki ba kan tarukan addinin islama yadda kasar nan ta shiga cikin kungiyar kima shine abinda buhari ya fara bayan karbar rantsuwa .
Shin Wanda ke tare da gwamnati suna sauraren wandan da suka zabe su? Shin ko Suna sauraran mutane ba muzgunawa ?
Munyi mamaki yadda shugaba Muhammad Buhari yayi hakan.
CAN tace ya kamata a rika sauraren Osinbajo da kima mukamin sa kan matsalar Fulani da kuma kokarin musuluntar da kasa .
Sannan dole ayi duba da maganar Obasanjo kan musuluntar da kasa da kuma Fulani.