- Gwamnan Cross Rivers Sanata Bassey Otu ya bayar da umarnin dakatar da daukar ma’aikata a jihar.
- An umurci dukkan ma’aikatan jihar da su mika kansu ga tantancewa da kuma takardun shaida.
- Tsohon gwamnan jihar Ben Ayade a karshen gwamnatinsa ya dage takunkumin da ya kakabawa aiki da kuma karin girma.
Gwamnan jihar Cross Rivers Sanata Bassey Otu ya bayar da umarnin dakatar da daukar ma’aikatan da ake ci gaba da yi a ma’aikatun gwamnati har sai an yi wata sanarwa nan gaba,kamar yadda Vanguard ta rawaito.
A wata sanarwar manema labarai mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran sa, Mista Emmanuel Ogbeche, Gwamna Otu ya kuma umurci dukkan ma’aikatan jihar da su mika kansu ga tantancewa da kuma takardun shaida.
KARANTA WANNAN: Gwamnan Jigawa Namadi Ya Yi Wasu Sabbin Nade-Nade
“A bisa bukatar gwamnatin jihar Kuros Ribas na sake mayar da ma’aikatan jihar don cimma manufofin gudanar da ayyukan yi na zamani, tare da baiwa gwamnati damar yin shiri yadda ya kamata domin amfanin ma’aikatanmu masu himma.
“Sanata Prince Bassey Edet Otu, Gwamnan Jihar Kuros Riba, ya amince da haka; cikakken sake tabbatar da ma’aikatan gwamnati a ma’aikatun gwamnati.
“Sake tabbatar da duk wani karin girma da aka yi a cikin watanni 6 da suka gabata da kuma dakatar da daukar ma’aikatan gwamnati da ake yi har sai anyi sabuwar sanarwa.
“Bada umarnin shine duk ma’aikatan gwamnati dole ne su gabatar da kansu don tantancewa da takardu a ofishin sakataren gwamnatin jihar a ranar da za a bayyana.
Ku tuna cewa tsohon gwamnan, Sanata Ben Ayade a karshen gwamnatinsa ya dage takunkumin da ya sanyawa aiki da karin girma.
A wani labarin kuma,NEMA Ta Karbi ‘Yan Najeriya 109 Da Suka Dawo Daga Kasar Libya
Hukumar NEMA, ta tabbatar da karbar wasu mutane 109 da suka dawo daga kasar Libya.
An taimaka wa wadanda abin ya shafa dawowa cikin kasar ta hanyar shiga tsakani na Hukumar Kula da Hijira ta Duniya.
An bukaci wadanda suka dawo da su yi amfani da damar domin zama jakadun albishir ga sauran matasa da ke shirin fita wata kasar.