Kungiyar Taliban ta mayar da martani kan ikirarin mayakan da ke da alaka da kungiyar IS, kan zargin da ake cewa, IS ta mamaye lardin Kunduz na kasar Afghanistan.
Hajji Najibullah Haron, babban jami’in leken asirin kungiyar Taliban ya ce, IS ba ta mamaye lardin Kunduz na arewacin Afghanistan ba.
Kamfanin Dillancin Labaran Nigeria NAN, ya ruwaito cewa,Haron ya bayyana rahotannin a matsayin marasa tushe da balantana makama.
Da yake yi wa manema labarai jawabi a ranar yau Laraba, ya ce: “Zaman lafiya na din-din-din ya dawo lardin Kunduz kuma mutane na zaune cikin kwanciyar hankali a can, kanazalika duk wani rahoto game da kasancewar yan ta’addar IS a Kunduz ba gaskiya bane.” a cewar shi.
KARANTA WANNAN LABARIN: Shin ko kunsan Manyan aiyukan Sanata Uba Sani?
Ya jaddada cewa sabuwar gwamnatin Afganistan, ba za ta bari kowa ya kawo cikas ga zaman lafiya da tsaro a Kunduz, ko wani yanki na kasar ba.
Kwanan nan kungiyar Taliban ta karbe ikon gwamnatin Afghanistan bayan ta karbe ikon Kabul Babban birnin kasar.
A wani labarin Kuma na daban
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rantsar da sabbin kwamishinonin guda uku na hukumar zabe mai zaman kanta INEC
An dai gudanar da bikin ne a takaice kafin fara gudanar da babban taron majalisar zartarwa ta tarayya FEC na mako a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Wadanda aka rantsar sun hadar da Dr Baba Bila mai wakiltar shiyyar Arewa maso Gabas, Farfesa Sani Adam, Arewa ta Tsakiya da Farfesa Abdullahi Abdu, mai wakiltar Arewa maso Yamma.
A halin yanzu Buhari yana jagorantar taron FEC na mako -mako a dakin taro na ofishin uwargidan shugaban kasa dake fadar sa.
Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osinbajo da Sakataren Gwamnatin Tarayya SGF, Mista Boss Mustapha, na cikin wadanda suka halacci taron.
Akwai kuma Ministan Yada Labarai da Al’adu, Lai Mohammed, Babban Lauyan Kasa kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, da kuma ministan Albarkatun Ruwa, Suleiman Adamu.
Sauran sun hada da ministan kasafin kudi da tsare -tsare na kasa, Misis Zainab Ahmed, da na Ayyuka da Gidaje, Babtunde Fashola, da ministan cikin gida Ogbeni Rauf Aregbeshola.
Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya, Dakta Folashade Yemi-Esan da sauran Ministoci da suka halarta.