Wasu matasa a garin Wukari ta Jihar Taraba sun fasa wani ofishin ‘yan sanda su ka saki wasu mutane uku da a ke zargi da kera bindigogi da ’yan sandan su ka kama. An kama mutanen uku ne a a garin na Wukari a ranar Lahadi bisa zargin da a ke yi mu su na kera bindigogi. ’Yan sandan sun ce a na kan shirin tafiya da mutanen uku da a ke zargin ne zuwa babban birnin jihar, wato Jalingo, a lokacin da matasan su ka dirga a ofishin ’yan sandan su ka fasa tare da sakin mutanan uku da a ke zargin. Wani ganau, wanda bai son a ambaci sunansa, ya shaida wa wakilinmu ta waya cewa, matasan sun fasa ofishin ‘yan sandan ne tare da lakadawa ’yan sandan da su ke a bakin aiki dukan tsiya, su ka kuma saki mutanan uku da a ke zargin da karfin tsiya. Idan dai ba a manta ba, matasa a yankin sun kone ofishin yanki na ‘yan sandan da ke cikin garin a lokacin da a ka yi hatsaniyar zabe ta shekarar 2013. Da wakilinmu ya tuntubi Kakakin rundunar ‘yan sandan na Jihar, DSP Dabid Misal, cewa ya yi, ba a kawo rahoton afkuwar lamarin ga hedikwatar rundunar ba tukunna, amma ya yi alkawarin tuntubar ofishin ‘yan sandan da ke Wukari domin jin gaskiyar abin da ya auku din. “Har yanzun mu na jiran jin abin da ya faru ne daga babban jami’in ‘yan sanda na yankin tukunna,” in ji Kakakin ‘yan sandan a martanin sakon da wakilin namu ya aike ma sa da shi ta wayar hannu.