• About Us
  • Blog
  • Gwamnatin Jihar Kano ta ce ana gabda fara ginin masana’antun Iskar Gas a Jihar
  • Home
Monday, March 20, 2023
  • Login
Dimokuradiyya
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
Dimokuradiyya
No Result
View All Result
Home Labarai

Tarihin Mohammed Morsi yana cewa ‘Ni aka zalunta’

Mustapha Haruna Dabai by Mustapha Haruna Dabai
June 18, 2019
in Labarai
Reading Time: 3 mins read
1 0
0
2
SHARES
15
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Mohammed Morsi shi ne zababben shugaban kasar Masar na farko, wanda sojoji suka hambarar bayan shekara daya kawai a kan mulkin a ranar 3 ga watan Yulin 2013.

Yunkurin sojojin ya biyo bayan zanga-zangar da ‘yan kasar suka shafe kwanaki suna yi da kuma bijire wa umarni sojojin da ya yi na ya kawo karshen halin da siyasar kasar ta shiga a lokacin bayan tumbuke Hosni Mubarak a shekarar 2011.

Wata hudu bayan hambarar da shi aka gurfanar da shi a gaban kotu tare da sauran mutum 14 na kungiyar ‘Yan’uwa Musulmi ta Muslim Brotherhood, inda aka zarge su da iza magoya bayansu wajen kisan masu zanga-zanga.

Haka zalika an kuma zarge su da tsarewa tare da azabtar da wasu daga cikin masu zanga-zangar.

Zarge-zargen sun danganci gwabzawa da aka yi tsakanin magoya bayan ‘yan adawa da kuma magoya bayan jam’iyyar Brotherhood a wajen fadar shugaban kasa ta Ittihadiya da ke Alkahira a 2012.

A zaman kotun na farko, Morsi ya daga murya daga cikin kejin da ake tsare da shi a cikin kotu yana mai cewa shi “Ni aka zalunta da juyin mulki” sannan kuma ya yi watsi da ikon kotun na shari’ar da take yi masa.

An wanke shi daga zargin kisan kai amma an daure shi shekara 20 bisa umarnin da ya bayar wajen tsarewa da kuma azabtar da masu zanga-zanga.

Daga baya kuma aka yanke masa hukuncin kisa bayan tuhumarsa da wasu karin laifukan, kafin daga bisani a janye hukuncin.

Ya rasu ne yayin da ake tsaka da yi masa shari’a a harabar kotu ranar 17 ga watan Yunin 2019.

Dan majalisar ‘Yan‘uwa Musulmi

Karan Morsi ya kai tsaiko a kungiyar ‘Yan’uwa Musulmi bayan ya zama dan majalisar kasa a matsayin Indifenda daga shekara ta 2000 zuwa 2005.

A matsayin dan majalisa, an sha yabonsa kan yadda yake da fasahar iya zance, kamar yadda ya yi a 2002 lokacin da aka samu hatsarin jirgin kasa, inda ya soki gazawar gwamnati.

An zabe shi a matsayin dan takarar jam’iyyar ‘Yan’uwa Musulmi a watan Afrilun 2012 bayan mataimakin shugaban jam’iyyar kuma hamshakin dan kasuwa Khairat al-Shater ya ajiye aikinsa.

A yayin kamfe dinsa, Morsi ya gabatar da kansa a matsayin wani bango da zai dakile duk wani yunkuri na dawo da salon tsohuwar gwamnatin Hosni Mubarak.

Juyin mulki

Sojoji sun gargadi Morsi cewa za su shiga cikin rikicin matukar bai gamsar da ‘yan kasa ba, kuma suka ba shi kwana biyu a matsayin wa’adi.

A yammacin 3 ga watan Yuli, sojoji suka dakatar da kundin tsarin mulkin kasar sannan suka sanar da kafa wata kwarya-kwaryar gwamnatin kwararru ta wucin-gadi kafin sabon zabe.

Morsi ya yi Allah-wadai da wannan yunkuri a matsayin juyin mulki.

Shugaban sojin kasar, wanda shi ne shugaban kasar a yanzu Abdul Fattah al-Sisi, shi ne ya ba da umarnin kama shi.

Sojoji sun tafi da shi zuwa wani boyayyen wuri, inda aka shafe mako biyu ba tare da jin duriyarsa.

An haifi Morsi ne a kauyen El-Adwah a gabar kogin Nilu a lardin Sharqiya a shekarar 1951.

Ya yi karatu a fannin injiniya a Jami’ar birnin Alkahira a shekarun 1970 kafin ya tafi kasar Amurka, inda ya kammala digiri na uku a can.

Bayan da ya samu nasara a zaben 2012, ya yi alkawarin cewa “gwamnatinsa za ta tafi da duka ‘yan Masar”.

Sai dai masu suka sun ce gwamnatinsa ta kasa cirewa ‘yan kasar kitse a wuta.

An yi zarginsa da barin masu tsananin kishin addinin Islama cin karensu babu babbaka a fagen siyasar kasar da rashin iya tafiyar da tattalin arzikin kasar.

Previous Post

Madrid ta taya Salah £150m, Barca na son Rashford

Next Post

Sojoji na horar da jami’an Kwastam sarrafa makamai a Bauchi

Next Post

Sojoji na horar da jami’an Kwastam sarrafa makamai a Bauchi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result
Arabic Arabic English English French French Hausa Hausa
  • Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    2455 shares
    Share 982 Tweet 614
  • Da Ɗumi-Ɗuminsa: Ƙazamin Rikici Ya Kaure Tsakanin Shugaban Ƙungiyar CAN Da Isa Ashiru Kudan

    1995 shares
    Share 798 Tweet 499
  • Sai na yi lalata da kai na kwanaki 4 babu ƙaƙƙautawa sannan zan taimaka maka, Wata mata ga saurayi

    1693 shares
    Share 677 Tweet 423
  • Ga Irinta Nan: Budurwa Ta Koka Bayan Saurayinta Ya Ƙi Amsar Cikin Da Ya Ɗirka Mata

    1365 shares
    Share 546 Tweet 341
  • CBN Ya Sake Fitar Da Sabbin Bayani Kan Dawo Da Tsofaffin Takardun Kudin Naira

    1592 shares
    Share 637 Tweet 398
Yanzu-Yanzu: Zanga-zangar Karancin Kudin Naira Tana Cigaba Da Yaduwa

DA DUMI-DUMINSA: Jam’iyyar APC Ta Lashe Zaben Gwamnan Jihar Ebonyi

March 20, 2023
Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

March 20, 2023
INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

March 20, 2023
PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

March 20, 2023
Bayan Faduwa A Zaben Sake Darewa Kujerar Sanata Nnamani Ya Bar PDP

Bayan Faduwa A Zaben Sake Darewa Kujerar Sanata Nnamani Ya Bar PDP

March 20, 2023
Mohammed Ya Sake Lashe Zaben Gwamna Karo Na Biyu A jihar Bauchi

Mohammed Ya Sake Lashe Zaben Gwamna Karo Na Biyu A jihar Bauchi

March 20, 2023
Yanzu-Yanzu: Zanga-zangar Karancin Kudin Naira Tana Cigaba Da Yaduwa
Labarai

DA DUMI-DUMINSA: Jam’iyyar APC Ta Lashe Zaben Gwamnan Jihar Ebonyi

March 20, 2023
Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe
Labarai

Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

March 20, 2023
INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato
Labarai

INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

March 20, 2023
Yanzu-Yanzu: Zanga-zangar Karancin Kudin Naira Tana Cigaba Da Yaduwa

DA DUMI-DUMINSA: Jam’iyyar APC Ta Lashe Zaben Gwamnan Jihar Ebonyi

March 20, 2023
Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

March 20, 2023
INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

March 20, 2023

Twitter

Archives

Recent Posts

  • DA DUMI-DUMINSA: Jam’iyyar APC Ta Lashe Zaben Gwamnan Jihar Ebonyi
  • Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe
  • INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

Quick Links

  • Tsaro
  • Siyasa
  • Labarai
  • Wasanni
  • Kasuwanci
  • Rikicin Duniya

Contact Us

info@dimokuradiyya.com.ng

0809 912 4425 +234 809 912 4425

No. 218 Mogadishu layout Kaduna City Center Ahmadu Bello way kaduna. Kaduna, Nigeria 800273

Copyright © 2022 Dimokuradiyya Media Services LTD.

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio

Copyright © 2022 Dimokuradiyya Media Services LTD.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In