Kocin Manchester United Erik ten Hag ya yi karin haske dangane da yan wasan kungiyar dake fama da rauni gabanin wasan sh na ranar Laraba a gasar Premier League. Kamar yadda Daily Post ta ruwaito.
Antony ba zai samu fafata wasan ba bayan an cire shi a wasan da United ta sha da kyar a hannun Crystal Palace da ci 2-1 a ranar Asabar din da tagabata.
KARANTA WANNAN LABARIN: Jam’iyar PDP Ta Bukaci Goyon Bayan Yan jarida
Ten Hag ya kuma bayyana cewa Martial da Scott McTominay ba su murmure daga raunin da suke fama da shi ba.
“Martial da McTominay ba za su samu damar fafata wasan gobe ba.
“Kana Antony don Santos ba zai fafata wasan na ranar Laraba ba, don haka ya kamata musan mafita” inji Ten Hag.
A wani labari kuma, Da Dumi-Dumi: Masu Zanga-Zangar Sun Toshe Kofar Shiga CBN
Wata kungiyar farar hula a jihar Edo, Edo Civil Society Group karkashin jagorancin Kwamared Agho Omobude a ranar Talatar ta tare babbar kofar shiga babban bankin Najeriya da ke birnin Benin, sakamakon karancin kudaden Naira da ya janyo wa miliyoyin ‘yan Najeriya wahala.
Sakamakon zanga-zangar ya tilastawa motocin da suka bi titin Ring Road ta Akpakpava sauya hanya zuwa ta titin Igun -Sokponba kafin su hade da titin Ring Road.