Tinubu: Buhari zai miƙa Mulki ga wanda yafi dace wa ya Gaje shi — Inji Uzodimma
Gwamnan Jahar Imo Hope Uzodimma ya yabawa Sanata Bola Tinubu a vjsa sanun nasarar sa na zama Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a Jam’iyyar APC, yana mai cewa Shugaban Ƙasa Muhammadu zai mikawa wanda ya cancanta domin ya gaje shi.
Uzodimma wanda shine Shugaban Zaɓen Fidda Gwanin yayi kira ga ƴan Takarar Shugaban Ƙasa dasu yi aiki tukuru domin samun nasarar Tinubu a Shekarar 2023.
Ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar ya sanyawa hannu, ya baiwa Manema labaru a jiya.
KARANTA WANNAN LABARIN: Hatsarin Mota Ya Hallaka Mutane 7 a Osun
Daily Post ta ruwaito cewar Tinubu ya samu ƙuri’u 1,271 inda ya doke Rotimi Amaechi wanda ya samu ƙuri’u 316 da Mataimakin Shugaban Ƙasa wanda ya samu ƙuri’u 235 a ranar Laraba.
Sanarwar tace “a madadin Gwamnati da Al’ummar Jahar Imo, Ina taya Tsohon Gwamnan Jahar Lagos Asiwaju Bola Tinubu akan nasarar daya samu a zaɓen fidda Gwani na Shugaban Ƙasa na Jam’iyyar APC domin Babban Zaɓen Shekarar 2023.
Comments 1