Dan takarar gwamnan jam’iyyar APC a jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Bola Tinubu, shi ne ya fi cancanta a cikin duk ‘yan takarar da ke neman zama shugabannin Najeriya a 2023.
Sani, Sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya, ya ce Tinubu ya yi yaki kuma ya biya hakkin sa domin dora mulkin dimokuradiyya a kasar nan a yau yayin da sauran ‘yan takarar shugaban kasa suka kasance masu neman gafarar soji kawai.
KARANTA WANNAN LABARIN: Sama Da Mambobin APC 5000 Ne Suka Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar PDP A Kogi
A cewar mai fatan zama Gwamnan, Tinubu ne ya fi cancantar zama Shugaban Najeriya, domin yana da duk abin da zai ciyar da kasar nan zuwa ga matakin girma.
Sani ya bayyana hakan ne a wajen bikin karramawar kungiyar ‘yan asalin jihar Legas a jihar Kaduna, yayin bikin ‘Isokan Omo Eko Day’, a babban birnin jihar ranar Lahadi.
Ya ce, “Ba za ka iya kwatanta Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da sauran ‘yan takarar Shugaban kasa ba, domin babu inda aka same su a lokacin da Asiwaju da mutane irinmu suke fafutukar ganin an dora mulkin dimokradiyyar da muke ciki a yau.”
“Na san Asiwaju tun a shekarar 1992. Mun goyi bayan abokai saboda hukuncin daya muke da mu; hukunce-hukuncen bin doka da oda, hukuncin adalci da ‘yancin ‘yan Nijeriya. Mun yi gwagwarmaya tare domin dora mulkin dimokuradiyya a Najeriya.”
“Kada ’yan Najeriya su manta cewa dalilin da ya sa muke haduwa a nan mu yi tarayya cikin walwala shi ne sadaukarwa da wasu mutane suka yi. Don haka nake kira ga ’yan Najeriya da su marawa Asiwaju Tinubu baya ya zama Shugaban Najeriya. A cikin duk wadanda suka fafata, Tinubu ne ya fi cancanta.”
“Yawancin sauran ’yan takarar Shugaban kasa sun kasance masu neman afuwar sojoji a lokacin da Tinubu ke fafutukar tabbatar da dimokuradiyya, ba su taba goyon bayan bin doka da oda da adalci ba. Asiwaju bai yi gwagwarmayar mulkin dimokuradiyya kadai ba, ya kuma biya hakkinsa, hasali ma an tsare wasu daga cikin mu, an kuma tsananta musu.”
“A yau, muna da tsarin dimokuradiyyar da muka yi yaki a kai, na yi imanin cewa lokacin Asiwaju ne ya zama shugaban kasa mai girma domin yana da abin da ake bukata don ciyar da Najeriya gaba. Babu wani daga cikin sauran ‘yan takarar da ke da tarihin nasarorin da ya samu kuma mun yi imanin zai yi kyakkyawan aiki.”
Tun da farko a jawabinsa na maraba, shugaban riko na kungiyar ’yan asalin Jihar Legas, Sheriff Olutusin, ya ce Tinubu ya gina ababen more rayuwa, masu ilimi, ya mayar da magudanar ruwa zuwa birane da kuma fadada kudaden shigar Legas daga Naira miliyan 600 zuwa Naira biliyan 50 da dai sauransu, kuma zai iya yin duk abin da ya faru dama kari idan aka bashi damar jagorantar Najeriya.
A wani labarin kuma, 2023: Ban Janye Daga Takarar Shugaban Kasa Ba – Tinubu Ya Magantu
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya musanta janyewa daga takarar shugaban Kasa.
Tinubu ya saka wani dan gajeren hoton bidiyonsa a kan wani shafi a yammacin ranar Lahadin nan, a wani yunkuri na karyata jita-jitar da ake yadawa.