Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Tinubu, ya gana da wasu fitattun gwamnoni da jiga-jigan jam’iyyar APC a sirrance.
Taron wanda ya gudana a gidansa da ke Abuja, ya samu halartar tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Adams Oshiomhole; Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai; Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle; Sakataren jam’iyyar APC na kasa, Iyiola Omisore, da mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Kashim Shettima ne suka halarta.
Ko da yake ba a bayyana cikakken bayani kan taron ba, wata majiya ta shaida wa wakilinmu cewa, sun tattauna ne a kan batun tikitin takarar Musulmi da Musulmi da ake takaddama a kai da kuma bukatar a nada wanda ya cancanta ya jagoranci kwamitin yakin neman zaben dan takarar jam’iyyar APC.
KARANTA WANNAN LABARIN: NLC ta baiwa FG wa’adin Makwanni biyu, ku ta tsumduma yajin aikin gama gari
A halin da ake ciki, kungiyar yakin neman zaben Tinubu, a ranar Talata, ta bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Legas ya bude tattaunawa da kungiyoyin addini da masu ruwa da tsaki a kasar.
Daraktan yada labarai da sadarwa na Tinubun, Bayo Onanuga, ya tabbatar da cewa shugaban nasa ya fara tuntubar masu ruwa da tsaki da suka hada da kungiyoyin addini gabanin fara yakin neman zabe na watan Satumba.
Onanuga ya kuma kara da cewa dalilin da ya sa mutane da yawa ba su san matakin na baya-bayan nan ba shi ne saboda an yi shirin kada a buga shi a kafafen yada labarai.