Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya nada gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni a matsayin mai ba shi shawara na musamman kan hadin kan Jam’iyyar “Integration and Reintegration Party” a taron yakin neman zaben shugaban kasa na Tinubu/Shettima.
A cikin wata wasika da Tinubu ya aike wa Buni kuma da kansa ya sanya wa hannu, dan takarar jam’iyyar APC ya ce “nadin ya dace ” ganin irin nasarorin da Buni ya samu a siyasance da kuma kyakkyawan shugabanci da ya nuna a matsayinsa na gwamnan jihar Yobe da kuma a matsayinsa na dan jam’iyya.
KARANTA WANNAN LABARIN: Najeriya @62: Buhari Bai Barwa ‘Yan Najeriya Abin Da Zasu Yi Murna Dashi Ba – LP
“Muna godiya da ka shiga kungiyar yakin neman zaben mu. Mun san za ku yi iya bakin kokarinku kan wannan sabon nauyi da aka dora muku domin mu gudanar da yakin neman zabe mai inganci, wanda zai kai mu ga nasara a zaben shugaban kasa na 2023.”
“Tare, ba wai kawai za mu iya tabbatar da nasarar jam’iyyarmu a zaben Fabrairu 2023 ba, har ma za mu ciyar da Nijeriya kan tafarkin daukakar kasa ta hanyar gina nasarorin da jam’iyyarmu da gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari suka samu wajen samar da kyakkyawan shugabanci ga ‘yan Nijeriya.” Tinubu ya kara da cewa.
A wani labarin kuma, Gwamnatin Borno Ta Gudanar Da Faretin Samun ‘Yancin Kai Na Farko Bayan Shekaru 12
A ranar Asabar ne gwamnatin jihar Borno ta gudanar da bikin cikar Najeriya shekaru 62 da samun ‘yancin kai, inda aka gudanar da fareti na farko cikin shekaru 12 da fara rikicin Boko Haram.
Gwamna Babagana Zulum ne ya jagoranci bikin da aka gudanar a dandalin Ramat da ke Maiduguri.