Tinubu zai kawo ƙuri’un Inyamurai dana yankin Kudu-maso-Gabas – Umahi
Gwamna David Umahi na jihar Ebonyi ya ba da tabbacin cewa jam’iyyar All Progressives Congress, APC, da ɗan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu za ta cinye ƙuri’un ‘yan kabilar Igbo idan aka zabe shi.
Ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da yake kaddamar da masaukin Gwamnan Ebonyi a ranar Laraba a Abuja.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ku ba mu Jirgin Tucano da Sojoji mu yaƙi Ƴan Ta’adda — Ayade zuwa FG
Umahi ya tabbatar wa Tinubu cewa shiyyar Kudu maso Gabas za ta zabi APC a 2023.
Ya ce wannan tabbacin ya nuna matsayin sauran gwamnonin Kudu maso Gabas.
Gwamnan ya kuma yi wa Tinubu alkawarin gudanar da gagarumin gangamin yakin neman zaben shugaban kasa a jihar.
“Don haka muna maraba da Asiwaju da gwamnoni jihar Ebonyi domin uwar duk wani taro. Girmanka, za ka ga abin da injiniya zai iya yi idan ka zo.
“Ba muna fakewa ba ne mu ce kai ne dan takararmu, kuma za ka kula da mutanen Kudu maso Gabas, kuma duk kuri’unmu za su tafi APC. Babu kuskure akan hakan.
“Don haka mutanen Kudu-maso-Gabas, mun yi magana. Ni ne Shugaban kungiyar Gwamnonin Kudu maso Gabas, don haka ina magana a madadinsu,” inji shi.
Gwamnan ya ce yankin Kudu-maso-Gabas zai ci gaba da zama da APC a 2023 domin “zai fi mana kyau
A wani labarin kuma: Babachir Lawal, Dogara: Masu suka na sun so su zama Mataimakina – Tinubu
Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa na Jam’iyyar All Progressives Congress, APC, Bola Tinubu, ya zargi wadanda ke sukar zabin Kashim Shettima a matsayin abokin takarar sa da neman a naɗa su a matsayin.
Tinubu ya ce wasu daga cikin wadanda ke sukar zaben Shettima a matsayin abokin takararsa, abokansa ne na kut-da-kut.