Dan majalisar na yin wannan maganar ne a matsayin martani ga jawabin ministan da aka ruwaito yana cewa; ‘titunan Nijeriya ba su lalace ba kamar yadda ake nunawa.’ Inda ya nemi Fashola da ya nemi gafarar Allah da na ‘yan Nijeriya bisa gazawarsa na gyaran munanan titunan kasarnan.
Dan majalisar tarayya mai wakiltar Idanre/Ifedore, Tajudeen Adefisoye ya shawarci ministan ayyuka Babatunde Fashola da ya ayyana dokar ta baci a dukkanin titunan gwamnatin tarayya dake fadin kasarnan.
Adefisoye, ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a a wata sanarwa da ya fitar a garin Akure wanda Kakinsa, Oluyemi Fasipe ya sanyawa hannu, inda ya nemi ministan da ya yi tafiya ta titunan Nijeriya har na tsawon wata shida domin gane wa idonsa tare da fuskantar abin da ‘yan Nijeriya ke fuskanta a kan titunan a kowacce rana.
Adefisoye, shi ne mataimakin Kwamitin soji na majalisar, ya ce Fashola bai san yadda titunan Nijeriya suke ba, saboda koyaushe a cewar dan majalisar Fashola na yawo ne a jiragen sama a duk inda za shi a kasarnan.
Ya ce; akwai bukatar ministan ya yi yawo kan titunan Nijeriya a dukkanin yankuna shida na kasarnan har na tsawon wata shida. Dan majalisar ya ce da yawan ‘yan Nijeriya sun rasa rayukansu sakamakon lalacewar titunan Nijeriya.
Sannan ya nuna yadda yanzu bata gari suka bata titunan kasar ta hanyar garkuwa da jama’a, yi musu fashi tare da kashe su. Ya ce yana da wuyan gaske mutum ya bugi kirji ya ce titunan Nijeriya garau suke.
Adefisoye ya bayyana titunan gwamnatin tarayya da suke mafi muni wanda ya hada da titunan Akure- Owo Road, Ibadan -Oyo -Ogbomoso Road da Owo-Akoko Road.
Sauran sun hada da Biu – Gombe road, Oyo- Iseyin road, Gboko -Katsina Alla-Zaki Biam Road, Lagos -Badagry Road, Asaba – Enugu Road da sauran su.