Sarakunan gargajiya na kasar Bassa dake Nijeriya, sun jinjinawa sojojin Nijeriya bisa nasarar da suke samu wajen yaki da ta’addanci a arewa maso gabashin Nijeriya da wadansu sassan kasar ma dake fuskantar matsalolin tsaro.
Sarakunan gargajiyar, da shugabannin yankin sun jinjinawa sojojin ne a Abuja, a yayin da suka kai wa Babban Hafsan sojin kasar, Laftanar Janar Tukur Buratai ziyara a ofishinsa dake Abuja a ranar Talata.
Shugaban sashen tsare-tsare na sojin, Laftanar Janar Lamidi Adeosun, shi ne ya karbi bakuncin Sarakunan da shugabannin a madadin shugaban sojojin.
Tawagar wanda Aguma na Bassa-Benin, Alhaji Bako Dogwo, ya jagoranta, har wala yau sun bai wai Buratai Sarautar gargajiya ta ‘Bijeshi’ wato ma’ana ‘Jarumi’ da yaren Bassa.
A yayin da yake bayyana makadusin ziyarar, Dogwo ya ce sun kawo ziyara Hedikwatar sojojin ne domin bayyana gamsuwar al’ummar Bassa ga sojojin Nijeriya bisa yadda suke magance matsalolin tsaron kasar.
Sarkin ya ce al’ummar Bassa Jarumai ne da suka san muhimmanci tsaro, ya ce shiyasa ma suka zo jinjina masa bisa abin da ya yi Nijeriya ta fuskancin tsaro. Ya ce al’ummar Bassa sun fi sama da miliyan Tara a sassan Nijeriya a jihohi 10 da suka hada da Kogi, Binuwe, Edo, Filato, Neja, Abuja da sauran su.
Sarkin ya yi amfani da wannan damar wajen kira ga hukumomin sojojin da su rika bai wa matasan Bassa damar shiga ayyukan soji, domin a cewarsa ta wannan fuskancin, ana barin matasan su a baya wajen ba su aiki a sojin.