A halin da ake ciki, wani jigo a jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Gbenga Olawepo-Hashim ya bukaci gwamnatin tarayya da ta dauki matsalar rashin tsaro a kasar nan da muhimmanci fiye da zaben 2023.
Olawepo-Hashim, a wata sanarwa da ya fitar daga ofishin yada labaransa a Abuja jiya, ya ce tilas ne ‘yan Najeriya su kasance da rai da lafiya kafin su iya kada kuri’a.
“A cikin shekaru biyu da suka gabata, mun yi magana a kan kalubalen tsaron da kasar nan ke fuskanta tare da bayar da shawarwari na musamman kan yadda za a tinkari su, amma duk shawarwarin da muka bada an yi watsi da su.
“Lokaci ya yi da a gina sabon tsarin tsaro don gyara irin barnar da hare-haren ta’addanci ya haifar da kawar da ‘yan fashi da garkuwa da mutane a fadin kasar nan,” in ji shi.
Kowa Ta shi Ta Fisshe Shi: Ba Mu Da ‘Dan Takara Ko Jam’iyya A Zaben 2023– INEC
“A cikin shekaru biyun da suka gabata mun yi magana kan kalubalen tsaron da kasar nan ke fuskanta tare da bayar da shawarwari na musamman kan yadda za a tunkari su, amma duk shawarwarin an yi watsi da su.
“Yanzu ne lokacin da ya kamata ‘yan kishin kasa da abokan arziki na Nijeriya su tashi tsaye wajen kare manufofin jamhuriyarmu, da akidar zaman lafiya, da manufofin zamani da wayewa.