Wasu masu ibada su bakwai hukumar kashe gobara da kiyaye hadura ta gwamnatin tarayya ta ceto rayuwarsu yayin da ginin majami’a ya rufta musu a yayin da suke tsaka da ibada a garin Ilori.
Rahotanni sun bayyana cewa ginin ya rufta ne a dalilin mamakon ruwan sama da aka yi a ranar Asabar.
Har wa yau, hukumar ta samu gawar wani matashi a wani gini da ya faɗo masa sakamakon tsawa mai ƙarfin gaske da ta kada ginin.
Sai dai akwai mutum ɗaya da har yanzu ba a ganin sakamakon awon gaba da ruwan saman yayi da shi.
Hukumar kashe gobara ta jihar Kwara ta tabbatar da faruwar lamarin ta hannun kakakin hukumar Mista Hassan Adekunle, idan ya shaidawa manema labarai cewa lamarin ya faru me da misalin ƙarfe 11:30 na daren ranar Asabar.