Kusan watanni goma sha shida da dakatar da tsohon Shugaban Hukumar EFCC daga bakin aiki, rahoto ya bayyana cewa har yanzu hukumar na biyan tsohon shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, Ibrahim Magu rabin albashin da yake dauka sanda yana shugabancin hukumar.
Jaridar Dimokuraɗiyya ta rawaito cewa, wannan ba wani sabon abu bane, domin kuwa idan aka yi duba Dangane da Dokokin Ma’aikatan Gwamnati, Magu yayin da ake tuhumar sa. rabi ne kawai zai samu daga cikin albashinsa har sai an yanke hukunci.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar da umarnin dakatar da Magu, daga mukamin sa tun a ranar 10 ga Yuli, 2020, bisa zargin cin hanci da rashawa da babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami, SAN ya yi masa.
Don haka ne Buhari ya kafa kwamitin shugaban kasa karkashin mai shari’a Ayo Salami domin gudanar da bincike kan zarge-zargen daban-daban da ake yi wa Magu.
Sai dai jinkirin fitar da rahoton kwamitin da shugaban kasa ya kafa. Yana kara haifar da wani shakku a zukatan yan kasar.
Da yake tsokaci kan lamarin a watan jiya, Ministan harkokin ‘yan sanda, Muhammad Dingyadi, ya ce tun bayan mika rahoton Salami ga shugaban kasa, ba a sake aikewa da ma’aikatar da kuma rundunar ‘yan sandan Najeriya ba.