Tsohon shugaban Najeriya, Dr Goodluck Jonathan, ya yi rashin kawunsa, Elder Omieworio Afeni.
Dan shekaru 87, Dattijo Afeni wanda ya rasu a Yenagoa, babban birnin jihar Bayelsa a karshen mako bayan gajeriyar jinya, shi ne kanin mahaifiyar Jonathan.
KARANTA WANNAN LABARIN: Rashin Tsaro: Shugaban INEC Ya Gana da NSA Gabanin Zaben 2023
Wata sanarwa da Ikechukwu Eze, mai baiwa Jonathan shawara kan harkokin yada labarai ya sanyawa hannu, ta bayyana cewa tsohon shugaban kasar ya tafi Bayelsa tun karshen makon da ya gabata lokacin da Mista Afeni ya rasu.
Sanarwar ta kuma ambato Jonathan yana cewa iyalin “sun yi baƙin ciki sosai da fitowar sa amma suna godiya ga Allah don baiwar rayuwa mai daɗi da ya bashi.”
Da yake bayyana marigayin a matsayin mutum mai gaskiya, wanda ke kawo zaman lafiya da hadin kai a tsakanin al’umma, Jonathan ya kara da cewa “Za a yi kewar dattijo Omieworio Afeni sosai saboda hikima da shawararsa ta hikima.”
An tsayar da jana’izar zuwa ranar 23 ga watan Maris, 2023 kuma dangi za su sanar da cikakkun bayanai game da shirye-shiryen jana’izar a kan lokaci.
A wani labarin kuma, Da Dumi-Dumi: Masu Zanga-Zanga Sun Toshe Kofar Shiga CBN
Wata kungiyar farar hula a jihar Edo, Edo Civil Society Group karkashin jagorancin Kwamared Agho Omobude a ranar Talatar ta tare babbar kofar shiga babban bankin Najeriya da ke birnin Benin, sakamakon karancin kudaden Naira da ya janyo wa miliyoyin ‘yan Najeriya wahala.
Sakamakon zanga-zangar ya tilastawa motocin da suka bi titin Ring Road ta Akpakpava sauya hanya zuwa ta titin Igun -Sokponba kafin su hade da titin Ring Road.
Masu zanga-zangar sun yi kira ga hukumar da ta dace da ta samar da sabbin takardun Naira domin rage radadin da ‘yan Najeriya ke fama da su a halin yanzu don samun kudadensu, yayin da suka bukaci CBN da ya fara bayar da takardun kudi na N100, N50 da N20 idan sabbin takardun sun yi karanci.