By Abbas Yakubu Yaura
Tsohon shugaban kasar Afirka ta Kudu, FW de Klerk, kuma bature na karshe da ya jagoranci kasar ya rasu yana da shekaru 85 a duniya.
Mista de Klerk, wanda kuma shi ne jigo a yunkurin da al’ummar kasar ke yi ga dimokuradiyya, ya kamu da cutar daji a bana, in ji kakakin sa.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa kafin rasuwar Mista de Klerk ya kasance shugaban kasar tsakanin watan Satumba na shekarar 1989 zuwa watan Mayu 1994.
A shekarar 1990 ya sanar da sakin jagoran adawa da wariyar launin fata, Nelson Mandela, wanda ya kai ga zaben jam’iyyu da dama a shekarar 1994.