Gwamnatin tarayya ta bayyana damuwa kan yawaitar mace-macen da ake samu a wasu jihohin kasar musamman na yankin arewa, wadanda tac e suna da nasaba da annobar korona, sai dai ba kai tsaye ba.
Yayin karin bayanin da ya saba yi a kowace rana kan halin da ake ciki dangane da yakar cutar korona a Abuja, Ministan Lafiyar, Dakta Osagie Ehanire, ya ce mafi akasarin mace-macen da aka samu a baya bayan nan cikin wasu jihohi, sun auku ne saboda tsoron zuwa asibiti da shiga zuciyoyin jama’a da dama, inda ya kamata su samu kulawa kan matsalar dake damunsu, to amma tun bayan bullar annobar COVID-19 da dama suka kauracewa asibitoci bisa fargabar ka da gwaji ya nuna sun kamu da cutar.
Har wala yau Ministan Lafiyar ya bayyana bakuwar halayyar kin karbar marasa lafiya ko ba su kulawa, da wasu jami’an lafiya ciki harda likitoci suka dauka saboda tsoron kamuwa da cutar Korona, a matsayin karin dalilin da ya janyo mutuwar mutane da dama cikin kankanin lokaci a sassan Nijeriya, ciki harda Jigawa, Kano, Yobe da kuma Azare dake Bauchi.