Gwamnatin Najeriya ta hannun Shugabar hukumar kula da yan Najeriya mazauna kasashen waje (NIDCOM), Honarabul Abike Dabiri-Erewa ta yabawa, Israel Adesanya bisa rike kambunsa na Unified Fighting Championship (UFC).
Adesanya, zakaran matsakaitan ajin ya samu nasarar kare kambunsa inda ya doke dan wasan Amurka Jared Cannonier a filin wasa na T-mobile da ke Las Vegas na kasar Amurka a Lahadi nan.
A cikin wata sanarwa da Mista Gabriel Odu na sashin yada labarai da hulda da jama’a na hukumar ya fitar, Dabiri-Erewa ya taya zakaran murnar samun gagarumar nasara inda ya doke abokin hamayyarsa Jared Cannonier ya ci gaba da rike kambun da ci 12-0.
Shugaban NIDCOM ta yaba da kwazon Adesanya tare da yaba masa saboda ya nuna ainihin ruhin Najeriya na “Kin Ci Gaba”.
Ta bukace shi da ya ci gaba da jajircewa da samun nasara ga Najeriya a Mixed Martial Art.
A wani labarin daban kuma
Hukumar kula da tekun bahar maliya ta kasar Masar ta bayar da umarnin rufe wasu bakin tekun Bahar Maliya a ranar Juma’a bayan da aka kashe wata mata ‘yar kasar Ostiriya mai shekaru 68 a wani harin da aka kai a safiyar wannan rana a gabar tekun Sahl Hasheesh, a cewar wasu majiyoyin tsaro biyu.
An kai wanda aka kashen zuwa wani asibiti mai zaman kansa bayan harin, kamar yadda wata majiya a Hukumar Kula da Lafiya ta Red Sea ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters. Ya kara da cewa, an yi yunkurin farfado da ita, amma ta mutu ne sakamakon gazawar jini, wanda hakan ya zama faduwa kwatsam da hawan jini sakamakon raunukan da ta samu da kuma zubar jini.
Majiyar tsaron ta kuma kara da cewa matar ta kasance a kasar Masar tsawon shekaru biyar tare da mijinta dan kasar Masar.